Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Christian Eriksen, ya amince cewa, ya na “bakin ciki” kan ficewar Cristiano Ronaldo daga kungiyar.
Duk da haka, Eriksen ya yarda cewa lokaci ya yi da kulob din zai ci gaba ba tare da dan wasan mai shekaru 37 ba.
Ronaldo ya amince da soke kwantiraginsa da United yayin gasar cin kofin duniya.
Ya kawo karshen zamansa na biyu a Old Trafford watanni shida kafin karshen kwantiraginsa.
“Muna bakin ciki cewa Ronaldo baya cikin sa.
“Abin da ya gada, sunansa a kowane kulob na musamman ne, don in yi sa’ar taka leda da shi a rayuwata ya yi kyau sosai. Kwallon yana ci gaba.
“Kuna jin cewa wasan na gaba bayan, mutane za su manta da yadda yake a da kuma yanzu hankalinmu ya kasance kamar ba ya nan,” in ji Eriksen.
United ta sake fara kamfen din ta na gida ba tare da Ronaldo ba, inda ta yi nasara a kan Burnley da Nottingham Forest.