fidelitybank

Ina bakin ciki a kan yadda ake yi wa ‘yan Najeriya kudin goro da sunan ‘yan damfara – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya koka kan yadda ake yi wa ƴan Najeriya kuɗin goro da sunan masu aikata laifuka ta intanet.

Ya ce irin wannan yana ɓata sunan akasarin al’ummar Najeriya da suke masu bin doka da oda. A cewar shugaban, an shafe tsawon shekaru ana yi wa ƴan Najeriya mummunar fahimta.

Shugaba Tinubu wanda ke birnin Paris na Faransa ya faɗi haka ne cikin wani jawabi da mataimakinsa Kashim Shettima ya gabatar.

Daga farkon shekarun 2000, ana kallon ƴan Najeriya a matsayin masu aikata ta’annati ta intanet – daga kutse da neman soyayya don samun kuɗi.

Tinubu ya ƙara da cewa alaƙanta laifukan intanet da al’ummar Najeriya ba shi da hujja kuma ba ya nuna yadda rayuwar ƴan Najeriya take waɗanda aka san su a matsayin jajirtattu da gaskiya sannan suna bayar da gudumawa ga ci gaban kasashe ta fannoni da dama daga batun ƙirƙirarriyar basira zuwa ga fannin lafiya.

A 2020 ne, hukumar binciken manyan laifuka a Amurka, FBI ta saka Najeriya a matsayin ta 16 a jerin ƙasashen da laifukan intanet ya fi shafa.

Laifukan intanet na janyo wa Najeriya asarar dala miliyan 500 kowace shekara, kamar yadda hukumar kula da harkokin sadarwa a Najeriya ta bayyana.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp