fidelitybank

Ina baiwa jam’iyyar APC hakuri da Tinubu – Ndume

Date:

Sanata Mohammed Ali Ndume ya nuna nadama tare da bayar da hakuri kan sukar da ya fito fili ya yi a kan jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya da kuma kasar Bola Ahmed Tinubu.

Sai dai a hirarsa da BBC, Sanatan ya ce sun nemi afuwar juna ne shi da jam’iyyarsa ta APC wadda ta ba da umarnin cire shi daga mukamin mai tsawatarwa a majalisar dattawa a watan jiya.

Ndume ya ce sun yi wata ganawa a jiya Talata da shugabannin jam’iyyar kuma ya nemi afuwa game da kalaman sukar da ya yi a kafafen yada labarai maimakon gabatar da koken nasa ga jam’iyyar.

Ya ce shi ma an ba shi hakuri kan abin da aka yi mishi ba tare da an gayyace shi ba, domin ji daga wajenshi.

Sai dai kuma Sanatan mai wakiltar Borno ta Kudu, ya ce har yanzu yana nan kan bakansa na magnaganun da ya yi domin magana ce da ya yi ta gaskiya, kuma saboda kishin kasa ba don wani abu na daban ba.

Sanatan ya ce akwai jam’iyyu kamar PDP ta SDP da wasu da suka fara zawarcinsa domin ya koma can domin ya yi musu takara a zaben 2027, saboda a cewarsa sun ga ba a mishi adalci ba dangane da abin da aka yi masa a APC.

To amma ya ce ai, ”mutum ba zai bar gidansa ya tafi wani waje ba.”

Dangane da tsohon mukamin nasa kuwa an ruwaito shugaban jami’iyyar ta APC Abdullahi Umar Ganduje na cewa za su rubuta wa majalisar dattawa kan ta sake duba maganar ta Ndume da nufin mayar masa da mukamin idan ta ga hakan zai yiwu.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp