Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jaddada cewa, bangaren zartarwa zai ci gaba da mutunta iyakokin da ke tsakaninsa da na shari’a kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.
Ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Malam Garba Shehu, ya aike wa manema labarai ranar Alhamis, a daidai lokacin da gwamnatinsa ta yi afuwa ga wasu tsoffin gwamnoni da aka kama da sace makudan kudaden jihohinsu.
Shugaban kasar ya yi wannan ikirari ne a yayin da ya karbi bakuncin shugabannin bangaren shari’a na kasar, domin yin buda-baki a fadarsa da ke Abuja.
“Ina mai tabbatar muku cewa ina matukar mutunta bangaren shari’a,” in ji Buhari yana mai karawa da cewa za a tabbatar da doka da oda a kasa ne kawai idan doka ta hau kan kowa ba tare da nuna bambanci ba.
“Ina yin kokarin nisanta kaina da ku saboda gudun zargin yin katsalandan,” a cewar Buhari inda ya ce ya gamsu da tsarin da kotuna suke bi wajen gudanar da shari’a.