Malam Muhammadu Sanusi II ya yi bayanin abin da ya kai shi ga rasa kujerar gwamnan CBN da sarauta sa.
Tsohon Sarkin ya yi wannan bayani ne a wajen rufe wani taro da aka shirya domin koyar da shugabanci. An yi wannan taron ne a birnin tarayya Abuja.
Sunusi na II Tsohon ya ce, fadawa masu mulki gaskiya ne dalilin da ya sa aka sauke shi daga matsayinsa.
A jawabinsa, tsohon gwamnan na CBN ya dauko abin da ya faru tsakanin mahaifinsa da Janar Murtala.
Jaridar Guardian ta rawaito, Muhammadu Sanusi II ya na cewa, karfin halinsa na fadawa masu mulki gaskiya ne ya rasa mukaman da ya rike a kasar nan.
Sanusi II ya koka da halin ma’aikatan da ake da su a yau, ya ce maimakon su rika bin ka’idar aiki domin kawo cigaba, mafi yawa sun sa abin Duniya a gaba.
“Ma’aikacin gwamnati yana yi wa kasar Najeriya aiki ne ba wani shugaban kasa, gwamna ko wani Minista ba.”
“An manta da wannan a kasar nan. Shiyasa bangarorin shari’a, kiwon lafiya, noman wuta da ilmi duk ba su aiki. Ina ba ku shawarar ku yi murabus, idan har ku na aiki, kuma ba za ku iya taimakawa mutanen da ya dace ba.” in ji Sanusi Lamido.