fidelitybank

Ina alfahari da harin da mayakan Hamas suka kai wa Yahudaw – Meshal

Date:

Tsohon shugaban ƙungiyar Hamas ya ce, yana alfahari da harin da mayaƙan Hamas suka kai Isra’ila a makon da ya gabata, yana mai cewa harin “yunƙuri ne na kawo ƙarshen mamayar Isra’ila”.

Yayin da yake magana gidan talbijin na Haberturk TV, shugaban hulda da ƙasashen ƙetare na ƙungiyar Hamas, Khalid Meshal ya ce rikici tsakanin Irsa’ila da Falasɗinu ya samo asali ne tun shekarar 1948, ba makon jiya ba.

“Isra’ila na cewa tana da ƙarfin soji, suna cewa ba za a ci galaba a kansu ba. Amma mun yi mamakin yadda aka ci galaba a kansu a makon da ya gabata,” in ji shi.

Da aka tambaye shi game da yadda mayaƙan Hamas ke kai wa fararen hula da ƙananan yara da tsofaffi hari, sai ya ce “Muna faɗa wa mayaƙanmu ka da su yi haka. To amma a lokutan yaƙi irin wadannan ala’umar kan faru. Ba wai yadda Isra’ila ke faɗa a koyaushe cewa ba ta kashe fararen hula”.

Da aka tambaye shi ko Hamas na aikata irin abin da take zargin Isra’ila da aikatawa? Mista Meshal ya ce “akwai babban bambanci”.

“Wannan ƙasarmu ce. Idan maƙiya suka zo daga waje, ko sojoji ko fararen hula, duk dai maƙiya ne, duk wanda ya zo ƙasarmu domin mamaya maƙiyinmu ne, kuma mai laifi”.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp