Wasu ‘yan bindiga sun kashe akalla mutane biyu a lokacin da suka kai farmaki garin Etekwuru mai cin gashin kansa a karamar hukumar Ohaji/Egbema ta jihar Imo.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na safiyar ranar Laraba.
Maharan sun kuma lalata kadarori tare da jikkata wasu mutanen kauyen kafin su bar yankin.
Wakilinmu ya rawaito mana cewa kawo iyanzu ba a iya gano dalilin kai harin ba, sai dai kuma al’umma na cikin fargaba a halin yanzu.
Haka zalika wakilin namu ya tabbatar mana da cewa, Sarkin yankin al’ummar, Eze Kenneth Okereke, ya tabbatar wa da wakilinmu harin da safiyar Laraba, ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su kai dauki ga mutanensa.