Asusun bayar da lamuni na duniya, IMF, ya bukaci babban bankin Najeriya da kuma gwamnatin kasar da su kara tsawon wa’adin daina amfani da tsofaffin kudin da aka sauya.
Hukumar ta IMF, ta yi kiran ne ‘yan sa’o’i bayan da Kotun Kolin Najeriya ta yanke hukuncin jingine wa’adin daina amfani da kudin na ranar 10 ga watan Fabrairu, har zuwa lokacin da za ta yi hukunci na karshe a ranar 15 ga watn na Fabrairu.
A wata sanarwa da asusun na IMF ya fitar yau Laraba, mai dauke da sa hannun wata jami’a, Laraba Bonet, ya ce ya yi kiran ne domin wahalar da ‘yan Najeriya suke sha.
Karanta Wannan:Â Da Dumi-Dumi: Kotu ta dakatar da CBN daga wa’adin karbar tsofaffin kudi
Sanarwar ta ce saboda irin wahalar da jama’a ke sha a harkokin kasuwancinsu da rayuwar yau da kullum saboda karancin sababbin takardun kudin na naira 1,000 da 500 da kuma 200, duk da matakan da Babban Bankin ya dauka, ya kamata hukumomin kasar su sauya shawara.
Hukumar IMF, ita ce ta farko cikin manyan hukumomin kudi na duniya da ta fito fili ta yi kiran tsawaita wa’adin daina amfani da tsofaffin kudin na naira.