fidelitybank

Ilimi ne zai fatattaki fatara da yunwa a Najeriya – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce ilimi da bunkasar sana’o’i ne mafita ga yunwa da fatara a Najeriya.

Ya bayyana hakan ne a wani taro da wata kungiya daga gidauniyar Bill & Melinda Gates a ranar Laraba a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Mista Rodger Voorhies, Shugaban Sashin Ci gaban Duniya da Dama na Gidauniyar ne ya jagoranci tafiyar.

Mataimakin shugaban kasa Shettima ya jaddada yadda sauyin yanayi ke shafar amfanin noma da kuma yadda yake da matukar muhimmanci wajen aiwatar da hanyoyin noman da suka dace domin tabbatar da wadatar abinci ga al’ummar Najeriya da ke kara fadada.

Don haka mataimakin shugaban kasar, ya roki gidauniyar Bill & Melinda Gates da ta kulla kawance tare da gwamnatin Najeriya domin bunkasa noman kasar, da inganta abinci mai gina jiki, da kuma karfafa tsarin ilimi.

Ya dorawa gidauniyar taimakawa ayyukan shugaban kasa Bola Tinubu da suka shafi karfafa jinsi, inda ya jaddada mahimmancin shirye-shirye da ya shafi yara mata ga kokarin Najeriya na rage talauci.

Mataimakin shugaban kasa Shettima ya mika godiyarsa kan irin gudunmawar da gidauniyar ke bayarwa a Najeriya, musamman a fannin kiwon lafiya a matakin farko da kuma kawar da cutar shan inna.

“Muna saka hannun jari sosai a kan sabbin hanyoyin noma da kuma mafi kyawun ayyukan noma don haɓaka yawan aiki.

“Duk da haka, muna buƙatar ƙwarewa da albarkatun gidauniyar Bill & Melinda Gates don haɓaka ci gabanmu,” in ji shi.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp