fidelitybank

Ilimi: Iyaye ku tura ‘ya’yan ku makarantun Islamiyya – Fa’izu Alfindki

Date:

Shugaban karamar hukumar birni da kewaye, Fa’izu Alfindiki, ya ziyarci makarantar Islamiyya dake Marmara, Kamaluddem Nama’aji Alfindiki School, wacce ta yi nasarar yaye dalibai 90 masu karatun Al-Qur’ani Maza da Mata.

Shugaban karamar hukumar Faizu Alfindiki, ya yabawa mahukuntan makarantar da iyaye bisa yadda suke sadaukar da lokacinsu da dukiyoyinsu wajen jawo ‘ya’yansu, domin samun ilimin addinin musulunci.

Ya ce “Ya na da matukar muhimmanci ba yara kadai ba, har ma da manya su ba da lokacinsu, domin samun ilimin addinin Musulunci, wanda zai samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma”. Inji shi

Shugaban karamar hukumar ya kuma yi kira ga iyaye da su tura ‘ya’yansu maza zuwa makarantar Islamiyya, ya na mai cewa abin takaici ne yadda akasarin daliban da suka yaye mata ne. Domin haka ya bukaci daliban da aka yaye da su ci gaba da yin biyayya ga iyayensu, tare da ba da lokacinsu wajen karatun Alkur’ani mai girma a kowane lokaci domin matasa su yi koyi da su.

Fa’izu Alfindiki ya kuma bayyana siyawa makarantar katafaren gida mai hawa biyu a dai-dai lokacin da makarantar ke cikin matsi na rashin isashshen wurin zaman dalibai.

Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero wanda ya jagorancin bikin yaye daliban, ya kuma yi kira ga daukacin malamai na addinin musulunci da limamai da su ba da lokacinsu wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...
X whatsapp