fidelitybank

Ilimi: Iyaye ku tura ‘ya’yan ku makarantun Islamiyya – Fa’izu Alfindki

Date:

Shugaban karamar hukumar birni da kewaye, Fa’izu Alfindiki, ya ziyarci makarantar Islamiyya dake Marmara, Kamaluddem Nama’aji Alfindiki School, wacce ta yi nasarar yaye dalibai 90 masu karatun Al-Qur’ani Maza da Mata.

Shugaban karamar hukumar Faizu Alfindiki, ya yabawa mahukuntan makarantar da iyaye bisa yadda suke sadaukar da lokacinsu da dukiyoyinsu wajen jawo ‘ya’yansu, domin samun ilimin addinin musulunci.

Ya ce “Ya na da matukar muhimmanci ba yara kadai ba, har ma da manya su ba da lokacinsu, domin samun ilimin addinin Musulunci, wanda zai samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma”. Inji shi

Shugaban karamar hukumar ya kuma yi kira ga iyaye da su tura ‘ya’yansu maza zuwa makarantar Islamiyya, ya na mai cewa abin takaici ne yadda akasarin daliban da suka yaye mata ne. Domin haka ya bukaci daliban da aka yaye da su ci gaba da yin biyayya ga iyayensu, tare da ba da lokacinsu wajen karatun Alkur’ani mai girma a kowane lokaci domin matasa su yi koyi da su.

Fa’izu Alfindiki ya kuma bayyana siyawa makarantar katafaren gida mai hawa biyu a dai-dai lokacin da makarantar ke cikin matsi na rashin isashshen wurin zaman dalibai.

Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero wanda ya jagorancin bikin yaye daliban, ya kuma yi kira ga daukacin malamai na addinin musulunci da limamai da su ba da lokacinsu wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...
X whatsapp