Shugaban karamar hukumar birni da kewaye, Fa’izu Alfindiki, ya ziyarci makarantar Islamiyya dake Marmara, Kamaluddem Nama’aji Alfindiki School, wacce ta yi nasarar yaye dalibai 90 masu karatun Al-Qur’ani Maza da Mata.
Shugaban karamar hukumar Faizu Alfindiki, ya yabawa mahukuntan makarantar da iyaye bisa yadda suke sadaukar da lokacinsu da dukiyoyinsu wajen jawo ‘ya’yansu, domin samun ilimin addinin musulunci.
Ya ce “Ya na da matukar muhimmanci ba yara kadai ba, har ma da manya su ba da lokacinsu, domin samun ilimin addinin Musulunci, wanda zai samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma”. Inji shi
Shugaban karamar hukumar ya kuma yi kira ga iyaye da su tura ‘ya’yansu maza zuwa makarantar Islamiyya, ya na mai cewa abin takaici ne yadda akasarin daliban da suka yaye mata ne. Domin haka ya bukaci daliban da aka yaye da su ci gaba da yin biyayya ga iyayensu, tare da ba da lokacinsu wajen karatun Alkur’ani mai girma a kowane lokaci domin matasa su yi koyi da su.
Fa’izu Alfindiki ya kuma bayyana siyawa makarantar katafaren gida mai hawa biyu a dai-dai lokacin da makarantar ke cikin matsi na rashin isashshen wurin zaman dalibai.
Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero wanda ya jagorancin bikin yaye daliban, ya kuma yi kira ga daukacin malamai na addinin musulunci da limamai da su ba da lokacinsu wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya.