fidelitybank

Ilimi: Dalibin Kano ya yi fintinkau a kasar Indiya

Date:

Wani dalibi dan jihar Kano da ke karatu a kasar Indiya, Abdulrazaq Nafiu Abubakar, mai shekaru 27, ya samu lambar yabo ta Vice Chancellor’s Gold Medal Award a kasar Indiya bayan da ya kammala karatunsa na farko a matsayin dalibin da ya fi kowa kwarewa a fannin fasaha a fannin Injiniya a Jami’ar Sharda ta kasar Indiya.

Abubakar daga karamar hukumar Nasarawa, wanda ya kamala karatun digiri na biyu da maki na CGPA 9.89 cikin 10.00 a kasar Indiya, ya karanta Mechatronics Engineering a Jami’ar Bayero ta Kano a lokacin da ya ke karatun digirinsa na farko, inda ya samu kyautar Ahmadu Adamu Muazu na 2019 a matsayin wanda ya fi kowa samun maki da CGPA 4.9 a tsangaya na Injiniya.

Bayan kammala karatunsa a shekarar 2019, matashin wanda ya kammala karatunsa ya samu gurbin karatu a kasashen waje ga dalibai 370 da suka kammala karatun digiri na farko a Kano, zuwa kasar Indiya domin samun digirinsa na biyu na Master’s na gidauniyar Kwankwasiyya.

Da a ka tambaye shi ta ya ya ya samu wannan nasara, sai ya ce”Duk abin yabo ya tabbata ga masu ba shi shawara wadanda su ka zaburar da shi tare da yi masa jagora har ya kai ga taron.

“To, babu abin da za a ce a kan yadda na fito a matsayin mafi kyawun ɗalibi, nufin Allah ne.

“Amma na san cewa na mai da hankali sosai a duk azuzuwan ilimi na, da kuma dakunan gwaje-gwaje,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa mafi yawan lokutan hutun sa ya na amfani da su ne wajen ayyuka da bincike, domin ya na da sha’awar koyon kere-keren fasahar zamani.

Nafi’u ya kuma yi nuni da cewa, daya daga cikin manyan kalubalen da ya fuskanta a lokacin da ya ke karatun digiri na farko shi ne wahalar samun bincike a fannin karatunsa, domin wani sabon shiri ne a lokacin.

Yayin tattaunawar sa da DailyTrust, ya bayyana karatu a Indiya a matsayin wani sabon al’amari wanda ya samu damar koyo daban-daban, amma ya kara da cewa, yin karatu a cikin sabon yanayi da kuma lokacin COVID-19 ya na da kalubale, kuma ya na da wahalar jurewa.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp