fidelitybank

Ilimi: Dalibin Kano ya yi fintinkau a kasar Indiya

Date:

Wani dalibi dan jihar Kano da ke karatu a kasar Indiya, Abdulrazaq Nafiu Abubakar, mai shekaru 27, ya samu lambar yabo ta Vice Chancellor’s Gold Medal Award a kasar Indiya bayan da ya kammala karatunsa na farko a matsayin dalibin da ya fi kowa kwarewa a fannin fasaha a fannin Injiniya a Jami’ar Sharda ta kasar Indiya.

Abubakar daga karamar hukumar Nasarawa, wanda ya kamala karatun digiri na biyu da maki na CGPA 9.89 cikin 10.00 a kasar Indiya, ya karanta Mechatronics Engineering a Jami’ar Bayero ta Kano a lokacin da ya ke karatun digirinsa na farko, inda ya samu kyautar Ahmadu Adamu Muazu na 2019 a matsayin wanda ya fi kowa samun maki da CGPA 4.9 a tsangaya na Injiniya.

Bayan kammala karatunsa a shekarar 2019, matashin wanda ya kammala karatunsa ya samu gurbin karatu a kasashen waje ga dalibai 370 da suka kammala karatun digiri na farko a Kano, zuwa kasar Indiya domin samun digirinsa na biyu na Master’s na gidauniyar Kwankwasiyya.

Da a ka tambaye shi ta ya ya ya samu wannan nasara, sai ya ce”Duk abin yabo ya tabbata ga masu ba shi shawara wadanda su ka zaburar da shi tare da yi masa jagora har ya kai ga taron.

“To, babu abin da za a ce a kan yadda na fito a matsayin mafi kyawun ɗalibi, nufin Allah ne.

“Amma na san cewa na mai da hankali sosai a duk azuzuwan ilimi na, da kuma dakunan gwaje-gwaje,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa mafi yawan lokutan hutun sa ya na amfani da su ne wajen ayyuka da bincike, domin ya na da sha’awar koyon kere-keren fasahar zamani.

Nafi’u ya kuma yi nuni da cewa, daya daga cikin manyan kalubalen da ya fuskanta a lokacin da ya ke karatun digiri na farko shi ne wahalar samun bincike a fannin karatunsa, domin wani sabon shiri ne a lokacin.

Yayin tattaunawar sa da DailyTrust, ya bayyana karatu a Indiya a matsayin wani sabon al’amari wanda ya samu damar koyo daban-daban, amma ya kara da cewa, yin karatu a cikin sabon yanayi da kuma lokacin COVID-19 ya na da kalubale, kuma ya na da wahalar jurewa.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...
X whatsapp