fidelitybank

Iheanacho zai buga gasar AFCON – Peseiro

Date:

Kocin Super Eagles, Jose Peseiro, ya ce a yanzu Kelechi Iheanacho ya samu cikakkiyar koshin lafiya don taka leda a gasar cin kofin Afirka na 2023, AFCON, a Cote d’Ivoire.

Paseiro ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da manema labarai a birnin Abu Dhabi na Hadaddiyar Daular Larabawa da yammacin jiya Litinin.

“Kelechi zai kasance tare da mu a Cote d’Ivoire. Ya gama jinyarsa a Leicester City,” inji shi.

A cewarsa, yanzu Iheanacho zai shiga cikin sauran ‘yan wasan Super Eagles a gasar AFCON bayan ya kammala jinyar raunin da ya samu a tsoka.

Iheanacho ya yi jinya saboda rauni kuma baya cikin atisayen kungiyar na tsawon mako guda a Abu Dhabi.

Dan wasan na Leicester City ya zauna a kulob dinsa domin ya murmure sosai a gasar AFCON da za a fara ranar Asabar a Abidjan na kasar Cote d’Ivoire.

A ranar Laraba ne ake sa ran Super Eagles wadda ta lashe kofin sau uku za ta tashi zuwa kasar Cote d’Ivoire domin halartar gasar cin kofin AFCON karo na 34 bayan halartar liyafar cin abinci ta musamman da Gwamna Babajide Sanwo-Olu zai shirya a Legas ranar Talata (yau).

A ranar 11 ga watan Fabrairu ne za a fara gasar AFCON na tsawon wata guda, inda ake sa ran Super Eagles za su fara fafatawar da Equatorial Guinea a filin wasa na Alassane Ouattara da ke Abidjan.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp