fidelitybank

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Date:

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya yi umarni a gudanar da cikakken bincike kan zarge-zargen da wani tsohon hafsan ƴansanda ya yi cikin wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, dangane da fanshon tsofaffin ƴansanda.

IGP ya umarci hukumar fanshon ƴansanda ta NPF da ta duba ƙorafin gaggawa, ta gano duk wata matsala, tare da ɗaukar matakin da ya dace don magance matsalolin da aka bayyana.

Kakakin rundunar ta ƙasa, ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja a ranar 26 ga Yuni, 2025.

A sanarwar, Egbetokun ya bayyana cewa rundunar ba za ta yi watsi da halin da tsofaffin jami’anta suke ciki ba, musamman duba da irin gudummawar da suka bayar wajen kare rayuka da dukiyar ƴanƙasa.

Ya ce walwala da jin daɗin jami’ai – masu aiki da waɗanda suka yi ritaya – na daga cikin manyan abubuwan da rundunar ke ɗauka da muhimmanci.

Ya ƙara da cewa biyan fansho cikin lokaci na da matuƙar tasiri wajen ƙarfafa gwiwa da mutuncin rundunar.

Ya kuma ce rundunar za ta ci gaba da sauraron ra’ayoyi da ƙorafe-ƙorafe domin inganta tsarin jin daɗin ma’aikata.

Ya ƙara da cewa NPF za ta haɗa kai da hukumomin da suka dace domin samar da mafita mai ɗorewa ga matsalolin da aka jero a cikin bidiyon.

Egbetokun ya kuma tabbatar wa da dukkan jami’ai – da masu aiki da waɗanda suka yi ritaya – cewa rundunar za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da ingantaccen tsarin walwala wanda zai dace da sadaukarwar da suka yi wa ƙasa.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp