fidelitybank

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Date:

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya yi umarni a gudanar da cikakken bincike kan zarge-zargen da wani tsohon hafsan ƴansanda ya yi cikin wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, dangane da fanshon tsofaffin ƴansanda.

IGP ya umarci hukumar fanshon ƴansanda ta NPF da ta duba ƙorafin gaggawa, ta gano duk wata matsala, tare da ɗaukar matakin da ya dace don magance matsalolin da aka bayyana.

Kakakin rundunar ta ƙasa, ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja a ranar 26 ga Yuni, 2025.

A sanarwar, Egbetokun ya bayyana cewa rundunar ba za ta yi watsi da halin da tsofaffin jami’anta suke ciki ba, musamman duba da irin gudummawar da suka bayar wajen kare rayuka da dukiyar ƴanƙasa.

Ya ce walwala da jin daɗin jami’ai – masu aiki da waɗanda suka yi ritaya – na daga cikin manyan abubuwan da rundunar ke ɗauka da muhimmanci.

Ya ƙara da cewa biyan fansho cikin lokaci na da matuƙar tasiri wajen ƙarfafa gwiwa da mutuncin rundunar.

Ya kuma ce rundunar za ta ci gaba da sauraron ra’ayoyi da ƙorafe-ƙorafe domin inganta tsarin jin daɗin ma’aikata.

Ya ƙara da cewa NPF za ta haɗa kai da hukumomin da suka dace domin samar da mafita mai ɗorewa ga matsalolin da aka jero a cikin bidiyon.

Egbetokun ya kuma tabbatar wa da dukkan jami’ai – da masu aiki da waɗanda suka yi ritaya – cewa rundunar za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da ingantaccen tsarin walwala wanda zai dace da sadaukarwar da suka yi wa ƙasa.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp