Hukumar kula da tarihin kwallon kafa da kididdiga ta duniya IFFHS, ta bayyana Vincent Enyeama, a matsayin gwarzon mai tsaron gida na Afirka a kowane lokaci.
IFFHS ta ayyana mai tsaron gida daga 1987 zuwa 2022.
An yi wannan matsayi ga dukkan nahiyoyi daban-daban da suka hada da Turai, Kudancin Amurka da Asiya.
An san Enyeama ne saboda bajintar da ya yi a lokacin da yake taka leda a Super Eagles.
Dan wasan ya kuma yi tasiri sosai a Enyimba ta lashe kofin zakarun nahiyar Afirka a 2003 da 2004.
Enyeama ya wakilci Najeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA uku a Koriya/Japan 2002, Afirka ta Kudu 2010 da Brazil 2014.
Haka kuma yana cikin kwallo ne a lokacin da Super Eagles ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka da aka yi a Afirka ta Kudu a 2013.