fidelitybank

Idan Ukraine ta harba mana makami mai dogon zango za mu magantu – Rasha

Date:

Rasha ta ce idan har Ukraine ta yi amfani da makaman Amurka masu cin dogon zango wajen kai mata hari, hakan zai matuƙar tayar da zaune tsaye.

Idan harin ya auku, zai zama karo na farko da “Amurka ta shiga cikin yaƙin dumu-dumu.”

Shugaban ƙasa Joe Biden ne ya sahale wa Ukraine amfani da makaman masu linzami domin kai hare-hare a Rasha, wanda ke zuwa kimanin wata biyu kafin ya sauka daga kujerar mulki.

Sai dai babu tabbaci ko an shawarci zaɓaɓɓen shugaban ƙasar, Donald Trump kafin a ɗauki wannan mataki.

Ukraine ta mallaki makamin US ATACMS, wanda ke cin zangon kilomita 300 da na Faransa wanda shi ma yake cin irin wannan zangon, amma ƙasashen yamma suka hana ƙasar amfani da su wajen kai wa Rasha hari.

Amma Biden yanzu ya sahale wa ƙasar amfani da makaman a yaƙin wanda aka fara a ranar 24 ga Fabrairun 2022.

Shugaban ƙasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce ba za a sanar da fara amfani da makaman ba, kawai za a ji su ne.

A lokacin yaƙin zaɓe, Trump ya yi alƙawarin kawo ƙarshen yaƙin cikin awa 24 idan ya zama shugaban ƙasa.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp