Sanata mai wakiltar Imo ta Yamma, Rochas Okorocha, a ranar Lahadi ya ce, idan har akwai yiwuwar samun tikiti da shi da Tinubu ya fito gabanin zaben shugaban kasa na 2023, zai yi nasara.
Okorocha ya jaddada yiwuwar kasancewa abokin takarar Bola Tinubu, jagoran jamâiyyar All Progressives Congress (APC) na kasa. Ya ce, hakan ya faru ne saboda yana wakiltar Kudu maso Gabas, yayin da Tinubu dan Kudu maso Yamma ne.
âNi da kawu Tinubu mun fi zama. Na san cewa a lokacin da ya dace yana iya zama saboda, shi ne ke tada zaune tsaye a Kudu maso Yamma kuma ni a Kudu maso Gabas nake.
âDon haka bari mu ga abin da ke faruwa a tsakaninmu, idan kuwa haka ne, zan roke shi ya dan sassauta domin mu ciyar da wannan sashe gaba,â in ji Sanatan a lokacin da yake gabatar da tambayoyi daga manema labarai a babban taron jamâiyyar na kasa da aka gudanar a Abuja.
Mista Okorocha ya kuma lura cewa mutane suna son sa saboda yana tausaya wa bil’adama kuma yana guje wa kabilanci.