fidelitybank

Idan PDP ta bukaci mu sasanta TNM ne za su duba batun – Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce har yanzu shi ɗan jam’iyyar PDP ne duk da cewa ya soma tattaunawa da jam’iyyar NNPP domin sauya sheka zuwa can.

A hirarsa da BBC, jagoran kungiyar siyasa ta Kwankwasiyya ya ce a makwannin da suka gabata ne suka kaddamar da wata sabuwar kungiya mai suna ‘The National Movement’, bayan nan ne aka samar da jam’iyyar NNPP wato New Nigeria People Party ma’ana dai sabuwar Najeriya.

Kwankwaso ya ce, wannan sabuwar jam’iyya ce ta mutanen da suka amince cewa akwai bukatar tsarin da aka taho da shi daga shekarar 1999 a sauya shi a kawo abin da jama’a za su amfana.

Ya ce, akwai bukatar nazari kan abin da kasa za ta sauya sannan ta samu sabon alkibla, sai dai yana mai jaddada cewa har yanzu ya na nan a cikin jam’iyyar PDP bai fita daga cikinta ba.

”A yanzu maganar da ake yi ina cikin jam’iyyar PDP, tun wancan lokacin mun fara abin hawa-hawa. Abu na farko da muka fara yi shi ne ja baya daga tsarin ta, tunanin wasu masu hankali za su zo a zauna a fada musu abin da ya dame mu amma jam’iyya ba ta yi ba, muka shiga kungiya nan ma ba a yi komai ba, to gamu a matakin jam’iyya. Har yanzu da na ke magana da kai muna tsakanin kungiya da jam’iyya sannan ban fita daga cikin jam’iyyar PDP ba, kuma wannan kungiya ta hade ne da jam’iyyar NNPP. Duk ranar da zan bar PDP ku ne na farko a za ku sani saboda abubuwan ne a tsare su ke mu na komai cikin tsanaki.”

Kwankwaso ya ce, ba wai ya raba kafa ba ne tsakanin jam’iyyar NNPP da PDP kuma idan manyan jam’iyyar PDP suka bukaci a sasanta tsakaninsu ya ce, yanayin zai danganta da abin da suka fada da kuma yadda su sauran abokan tafiya suka kalli lamarin.

”Maganar ba ta Rabi’u Kwankwaso ko ta Kwankwasiyya ba ce, magana ce ta ‘The National Movement’ kuma muna da yawa a ciki, sannan yawancin wadanda ke cikin ta manyan mutane ne dan haka ba zan yanke hukunci ni kaɗai ba.”

Da aka tambaye tsohon gwamnan kan rahotanni da ke cewa an rushe shugabancin jam’iyyar NNPP tun ma kafin su shige ta da kuma kakkabe duk wanda ba ɗan Kwankwasiyya ba da yin sabon zubi da ‘yan Kwankwasiyya sai ya kada baki ya ce:

”A’a ai jam’iyyar daman ba ta mu ba ce, amma ana son mu zo a tafi tare dan haka su na son mu kawo namu su ma su kawo nasu. Sannan lokacin shugabancinsu ya wuce don haka kowa ya sauka, ciki har da shugaban da ya yi mata rijista sama da shekara 20 da ta wuce. Dan haka tsari ne ake hadawa da namu da nasu saboda mafi yawan jihohi ba su da kowa,” in ji Kwankwaso.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp