Gwamnan jihar Rivers kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Nyesom Wike, a ranar Talata ya gargadi kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa (NWC) cewa, rashin tsayar da shi a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar zai janyo wa jam’iyyarbrashim nasara a 2023.
Ya kara da cewa, bayan da suka mara musu baya suka zama jam’iyyar ta tsaya, lokaci ne da za su mara masa baya ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.
Da yake magana yayin ziyarar tuntuba a kan NWC, gwamnan jihar Riverw ya ce, “sunan gidan yanzu Wike, domin haka kada ku yi kuskure ku rasa Wike.
Domin idan ka fadi Wike, ka fadi zabe. Ba fatan mu ba ne a ce mu fadi zabe.