Tsohon mai baiwa tsohon shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Reno Omokri, ya yi kira ga hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa, EFCC ta binciki mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo idan ya biya kudin fom din tsayawa takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.
A ranar Larabar da ta gabata ne jam’iyyar ta sanar cewa, fom din takarar shugaban kasa zai kasance Naira miliyan 100. Omokri, a ranar Alhamis, a cikin wata sanarwa ta kafofin yaɗa labarun, ya ce mataimakin, ta hanyar biyan albashin shekara, bai kamata ya iya biya ba.
“Albashin Osinbajo shi ne Naira 12 miliyan a kowace shekara. Ministoci suna samun rabin abin. Ta hanyar doka, ba za su iya samun kasuwancin gefe ba.”
“Don haka idan shi, ko Amaechi, ko Ngige, ko wani jami’in gwamnati ya sayi fom miliyan 100, EFCC ta binciki su”.
“Idan wata kungiya ta ce, tana bayar da gudummawar Naira miliyan 100 da Osinbajo, Amaechi, da Ngige, ko kuma wani jami’in gwamnati ke amfani da shi wajen siyan fom, irin wadannan kungiyoyin ya kamata INEC ta gurfanar da su gaban kuliya,bsaboda sun wuce ka’idojin da aka gindaya na bayar da gudummawar yakin neman zabe. !”, ya rubuta.