Gabanin zaben 2023, dan takarar shugaban kasa a karkashin jamâiyyar All Progressive Congress (APC) kuma gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi, ya yi alkawarin kawo sauyi a Najeriya fiye da yadda ya sauya jiharsa a matsayin gwamna idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.
Umahi ya bayyana hakan ne a ranar Lahadin a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Mista Francis Nwaze ya sanya wa hannu yayin da yake taya sabbin shugabannin jamâiyyarsa a karkashin, Sanata Abdullahi Adamu da aka zabe shi a matsayin shugaban jam’iyyar baki daya, bayan da wasu âyan takara shida suka janye daga takarar.
Kalamansa âAbin da na yi a jihar Ebonyi shi ne karamin abin da âyan Nijeriya za su yi tsammani idan Allah Ya kai ni a matsayin shugaban Najeriya na gaba.