fidelitybank

Idan na zama shugaba zan haɗa kai da Afrika ta Kudu – Atiku

Date:

Dan takarar shugabancin kasar nan na PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya karbi bakuncin Jakadan Afrika ta Kudu a Najeriya, Thamsanga Dennis Mseleku a gidan sa dake Asokoro.

Sanarwar mai kunshe da sa hannun Abdulrasheed Shehu, ya ce, tattaunawar ta su a yayin zaman ta mayar da hankali ne kan yadda za a fadada dangantakar difulomasiyya tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu, domin ya zama sanadiyyar karfafa dangantaka tsakanin kasashen Afrika da nufin samar da tsarin da ake bukata na gina hadin kai da tattalin arziki a Nahiyar.

Dennis Mseleku ya ce, Najeriya na bukatar Mika mulki cikin ruwan sanyi, inda ya yi alkawarin goyon baya daga kasar sa domin Najeriya ta samu gudanar da ingantaccen zabe a 2023. Ya yabawa kasashen biyu bisa yunkurin su na sake karfafa alaka, yana mai cewa abinda kasashen biyu suka fi bukata a yanzu shi ne aiki a zahiri domin inganta tattalin arziki.

A nasa bangaren, dan takarar shugabancin kasar na PDP, ya godewa Jakadan na Afrika ta Kudu bisa ziyarar, inda ya jinjina masa bisa kokarin kyautata alaka tsakanin Najeriya da kasar sa. Wazirin Adamawa ya kuma Yi alkawarin muddin an zabe shi shugaban kasa a 2023, zai yi aiki domin habaka dangantakar kasashen biyu domin saura su yi koyi.

Abdulrasheed Shehu
Mataimaki na Musamman ga Mai girma Atiku Abubakar kan kafafen yada labarai.

29 ga Yuli 2022.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp