Dan takarar shugabancin kasar nan na PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya karbi bakuncin Jakadan Afrika ta Kudu a Najeriya, Thamsanga Dennis Mseleku a gidan sa dake Asokoro.
Sanarwar mai kunshe da sa hannun Abdulrasheed Shehu, ya ce, tattaunawar ta su a yayin zaman ta mayar da hankali ne kan yadda za a fadada dangantakar difulomasiyya tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu, domin ya zama sanadiyyar karfafa dangantaka tsakanin kasashen Afrika da nufin samar da tsarin da ake bukata na gina hadin kai da tattalin arziki a Nahiyar.
Dennis Mseleku ya ce, Najeriya na bukatar Mika mulki cikin ruwan sanyi, inda ya yi alkawarin goyon baya daga kasar sa domin Najeriya ta samu gudanar da ingantaccen zabe a 2023. Ya yabawa kasashen biyu bisa yunkurin su na sake karfafa alaka, yana mai cewa abinda kasashen biyu suka fi bukata a yanzu shi ne aiki a zahiri domin inganta tattalin arziki.
A nasa bangaren, dan takarar shugabancin kasar na PDP, ya godewa Jakadan na Afrika ta Kudu bisa ziyarar, inda ya jinjina masa bisa kokarin kyautata alaka tsakanin Najeriya da kasar sa. Wazirin Adamawa ya kuma Yi alkawarin muddin an zabe shi shugaban kasa a 2023, zai yi aiki domin habaka dangantakar kasashen biyu domin saura su yi koyi.
Abdulrasheed Shehu
Mataimaki na Musamman ga Mai girma Atiku Abubakar kan kafafen yada labarai.
29 ga Yuli 2022.