fidelitybank

Idan na kasa gurfanar da Yahaya Bello zan yi murabus – shugaban EFCC

Date:

Shugaban hukumar EFCC da ke yaƙi da masu yi wa arzikin kasa zagon ƙasa, Ola Olukoyede ya sha alwashin yin murabus idan na gaza gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello.

A wani taron tattaunawa da zaɓaɓɓun editoci a hedikwatar hukumar da ke Abuja, babban birnin Najeriya, shugaban hukumar ya yi alƙawarin hukunta duk masu kawo kawo tarnaƙi ga kama tsohon gwamnan.

A ranar 18 ga watan Afrilu, EFCC ta ayyana Bello a matsayin wanda take nema ruwa a jallo saboda zarginsa da badaƙalar kuɗi ta naira miliyan 80.

Yahaya Bello dai bai bayyana gaban kotu ba tun bayan ayyana ana nemansa ruwa a jallo.

Shugaban EFCC ya ce da kansa ya kira Bello cikin mutunci inda ya nemi da ya bayyana gaban hukumar ya kuma yi bayani kan tuhume-tuhumen da ake masa.

Shugaban EFCC ya ce duk da kiran wayar, tsohon gwamnan bai amsa gayyatar ba.

Yahaya Bello dai ya musanta gayyatar da aka yi masa inda ya ƙalubalanci EFCC ta gabatar da kwafin takardar gayyatar da ta aike masa.

Cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran tsohon gwamnan ya fitar, Yahaya Bello ya zargi EFCC da yaɗa jita-jita.

Shugaban EFCC ya ce “Idan har ban ga ƙarshen binciken da ake yi wa Yahaya Bello ba, zan ajiye aikina a matsayin shugaban EFCC.

“Na gurfanar da tsoffin gwamnoni biyu da a yanzu aka ba su beli – Willie Obiano da Abdulfatah Ahmed. Da mun bi Bello tun Janairu amma muka jira umarnin kotu.

“Idan har na iya gurfanar da Obiano da Abdulfatah Ahmed da Chief Olu Agunloye, me zai sa ba zan gurafanar da Yahaya Bello ba?

Olukoyode ya kuma ce tsohon gwamnan ya kwashi dala dubu 720 daga asusun gwamnati kafin barin mulki domin biyan biyan kuɗin makarantar ɗansa.

Tsohon gwamna Bello ya roƙi babbar kotun tarayya a Abuja da ta soke izinin kama shi da aka bai wa EFCC ranar 17 ga watan Afrilu.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp