Kungiyar kwallon kafa ta kasa dake buga wasannin Olympics, za ta sami jimlar $ 20,000 kowannan su, idan sun doke Tanzaniya a farkon wasan su da za su fafata a ranar 23 a Dar es Salaam wato ranar Asabar.
Shugaban, hukumar kwallon kafa ta kasa bangaren kula da matasa, Aminu Baleele Kurfi ya yi sanarwar ne bayan da tawagar ‘yan wasan za su tattaki Tanzania.
‘Yan wasan da jami’an su sun tafi gabashin Afirka a daren Alhamis ta hanyar jirgin sama na Kenya ta jirgin sama.