fidelitybank

Idan Jonathan ya dawo APC zan yi ritaya daga siyasa – Vatsa

Date:

Jigon jam’iyyar APC a jihar Neja, Mista Jonathan Vatsa, ya sha alwashin ficewa daga jam’iyyar APC da harkokin siyasa, idan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya amince ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a karkashin jam’iyya mai mulki.

Ya ce tun a shekarar 2015 jam’iyyar APC mai mulki ta ci gaba da zargin Jonathan da jam’iyyar PDP a kan kalubalen da kasar ke fuskanta, amma yanzu suna shirin mayar masa da mulki.

Vatsa, tsohon kwamishinan yada labarai, al’adu da yawon bude ido na jihar Neja, ya ce idan Jonathan ya amince da matakin, zai amince da kalaman da wani tsohon gwamna ya yi cewa babu da’a a siyasa.

A cewarsa, “Ina addu’ar jita-jita ce kawai ko kuma labarin karya, amma idan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya amince ya tsaya takara a zabe mai zuwa kuma a karkashin jam’iyyar APC, to zan yarda da wani tsohon gwamna da ya taba cewa babu da’a a siyasa. Ba kawai zan bar jam’iyyar ba, zan bar siyasa in koma gona”.

Da yake mayar da martani ga labarin Jonathan ya fito takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar na jihar, ya ce yana sane da cewa jam’iyyar APC na da burin kada ta bar mulki ya koma jam’iyyar adawa ta PDP a 2023.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp