Jigon jam’iyyar APC a jihar Neja, Mista Jonathan Vatsa, ya sha alwashin ficewa daga jam’iyyar APC da harkokin siyasa, idan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya amince ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a karkashin jam’iyya mai mulki.
Ya ce tun a shekarar 2015 jam’iyyar APC mai mulki ta ci gaba da zargin Jonathan da jam’iyyar PDP a kan kalubalen da kasar ke fuskanta, amma yanzu suna shirin mayar masa da mulki.
Vatsa, tsohon kwamishinan yada labarai, al’adu da yawon bude ido na jihar Neja, ya ce idan Jonathan ya amince da matakin, zai amince da kalaman da wani tsohon gwamna ya yi cewa babu da’a a siyasa.
A cewarsa, “Ina addu’ar jita-jita ce kawai ko kuma labarin karya, amma idan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya amince ya tsaya takara a zabe mai zuwa kuma a karkashin jam’iyyar APC, to zan yarda da wani tsohon gwamna da ya taba cewa babu da’a a siyasa. Ba kawai zan bar jam’iyyar ba, zan bar siyasa in koma gona”.
Da yake mayar da martani ga labarin Jonathan ya fito takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar na jihar, ya ce yana sane da cewa jam’iyyar APC na da burin kada ta bar mulki ya koma jam’iyyar adawa ta PDP a 2023.