Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran za ta ɗora wa Amurka alhakin duk wani harin da Isra’ila ta kai kan cibiyoyin nukiliyarta.
Abbas Araghchi ya yi wannan gargaɗin ne bayan wani rahoto da kafafen yaɗa labaran Amurka suka fitar na cewa Isra’ila na shirin kai hari.
Ya zargi Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, da yunƙurin wargaza tattaunawar nukiliyar da ake yi tsakanin Amurka da Iran da za a ci gaba da zama a birnin Roma gobe Juma’a.
Wannan dai shi ne karo na biyar na ganawa tsakanin ɓangarorin biyu tun tsakiyar watan Afrilu.