Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bukaci kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP da su hada kai wajen ganin jam’iyyar ta samu nasara a 2023.
Atiku Abubakar a wata tattaunawa da ya yi da mambobin jam’iyyar, domin neman goyon bayansu kan burinsa na zama shugaban kasa a Abuja, ya ce, duk wani abin da bai kai ga nasara ba, ba zai yi wa jam’iyyar dadi ba.
Ya ce, zaben 2023 ya baiwa jam’iyyar damar komawa kan karagar mulki.
“Na damu kuma ya kamata ku ma ku damu cewa, idan ba mu yi nasara ba, hakan na nufin za mu sake tsayawa takara a cikin shekaru takwas masu zuwa.
“Nan da shekaru takwas masu zuwa, ban san adadin da za su rage a siyasa ba, kuma hakan na iya haifar da mutuwar jam’iyyar, saboda mutane suna jan hankali, musamman a kasashe masu tasowa, ga gwamnatoci.
Allah ya kawo Mana 🙏 dau