fidelitybank

Idan ana son zaman lafiya a PDP shugabanta ya yi murabus – Makinde

Date:

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya ce, mafita daya tilo daga cikin rashin fahimtar juna a jam’iyyar PDP shi ne shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorcha Ayu ya yi murabus.

Makinde ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a Ibadan.

Ya yi wannan jawabi ne a wata tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zabe mai zuwa na 2023, Abubakar Atiku da jiga-jigan jam’iyyar daga shiyyar Kudu maso Yamma.

DAILY POST ta rahoto cewa Atiku ya isa Ibadan ne tare da gwamnoni Ifeanyi Okowa na jihar Delta, da abokin takararsa, Aminu Tambuwal na Sokoto, Sanata Ademola Adeleke, Soji Adagunodo da Cif Raymond Dokpesi.

Sauran sun hada da tsohon gwamnan jihar Neja, Babangida Aliyu da takwarorinsa na Ondo, Olusegun Mimiko da Osun, Olagunsoye Oyinlola, Eyitayo Jegede, Dino Melaye da Ladi Adebutu.

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo da mataimakinsa Adebayo Lawal da kakakin majalisar dokokin jihar ne suka tarbi shugabannin PDP.

Makinde ya bayyana cewa dole ne jam’iyyar PDP ta gyara kanta kafin ta sake fasalin Najeriya.

Ya ce daya daga cikin sharuddan sake fasalin jam’iyyar shi ne Ayu ya yi murabus, yana mai bayanin cewa dan takarar shugaban kasa, Atiku dan Arewa ne yayin da Ayu kuma dan Arewa ne.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp