A ranar Lahadin nan da ta wuce, 31 ga watan Yuli 2022, Gwamnan Ribas watau Nyesom Wike, ya yi zama da mutanensa da jagororin jamâiyyar PDP.
Daily Trust ta rawaito cewa, Nyesom Wike, ya hadu da masu ruwa da tsaki a PDP da wadanda suka yi masa yakin neman tikiti na zaben 2023.
An yi wannan zama ne a gidan gwamnan Ribas da ke unguwar Asokoro a birnin tarayya Abuja.
KARANTA WANNAN:Â Rigimar PDP: Atiku makaryaci ne – Wike
An samu sabani tsakanin bangaren Gwamna Wike da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda ya sake samun tikitin takara a zaben badi.
Sai an yi waje da Ayu tukuna a wajen wannan taro da aka yi a Abuja, mutanen Wike sun bukaci a tsige shugaban PDP na kasa, Iyorchia Ayu, idan har ana so su goyi bayan Atiku Abubakar.