Hukumar ICPC reshen jihar Bauchi ta ce, ta kama wani mutum ɗauke da kuɗi da suka kai naira miliyan biyu, ciki da sababbi da kuma tsofaffin kuɗin da aka sauya.
Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce ta kama mutumin ne mai suna Hassan Ahmad da waɗannan kuɗaɗe duk da ƙaranci kuɗi da ake fama da shi.
“An kama shi da naira dubu ɗari tara na sababbin kudin da aka sauya, yayin da sauran naira miliyan ɗaya da dubu ɗari ɗaya suka kasance na tsofaffin kuɗi.
“An shirya kuɗin ne cikin irin jakar nan ta buhu, kuma tuni mutumin ya amsa laifinsa ya na cewa kudin zai kai su jihar Gombe ne ga wani ɗan siyasa.