Hukumar yaƙi da rashawa ta ICPC ta kasa, ta ce ta kama mawaƙin nan mai suna Oladipo Daniel Oyebanjo, wanda aka fi sani da D’Banj kan wani bincike da take yi wanda ya shafi kuɗaɗen shirin N-Power.
Wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na intanet ta ce ta kama D’Banj ne saboda ya ƙi martaba gayyatar da hukumar ta yi masa game da batun.
Sanarwar ta ce, ta gayyaci kimanin mutum 10 a cikin watannin da suka gabata a kan binciken da take yi game da badaƙala ta kuɗin N-Power, kuma tuni ta sake su, sai dai ta riƙe D’Banj bayan da ya kai kansa babban ofishin hukumar da ke Abuja a ranar Litinin saboda ƙin martaba gayyatar da ta yi masa a baya.
ICPC ta ce, yanzu haka mawaƙin na tsare a ofishinta kuma yana taimakawa a wajen binciken da ake yi.
Ta kuma ce, za ta tabbatar an hukunta duk mutane ko bankuna da suka taimaka wajen badaƙalar.