fidelitybank

ICPC ta kama mawaki D’Banj kan badakalar N-Power

Date:

Hukumar yaƙi da rashawa ta ICPC ta kasa, ta ce ta kama mawaƙin nan mai suna Oladipo Daniel Oyebanjo, wanda aka fi sani da D’Banj kan wani bincike da take yi wanda ya shafi kuɗaɗen shirin N-Power.

Wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na intanet ta ce ta kama D’Banj ne saboda ya ƙi martaba gayyatar da hukumar ta yi masa game da batun.

Sanarwar ta ce, ta gayyaci kimanin mutum 10 a cikin watannin da suka gabata a kan binciken da take yi game da badaƙala ta kuɗin N-Power, kuma tuni ta sake su, sai dai ta riƙe D’Banj bayan da ya kai kansa babban ofishin hukumar da ke Abuja a ranar Litinin saboda ƙin martaba gayyatar da ta yi masa a baya.

ICPC ta ce, yanzu haka mawaƙin na tsare a ofishinta kuma yana taimakawa a wajen binciken da ake yi.

Ta kuma ce, za ta tabbatar an hukunta duk mutane ko bankuna da suka taimaka wajen badaƙalar.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp