Pelumi Olajengbesi, lauya ga Oladapo Oyebanji, wanda aka fi sani da D’Banj, ya ci gaba da cewa, mawakin ba shi da wani laifi a kan duk zarge-zargen da hukumar yaki da cin hanci da rashawa (ICPC) ta yi masa.
Lauyan ya bukaci a saki D’Banj, yayin da ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta shiga cikin lamarin ta hanyar binciki zargin da ake masa.
Ya kuma kalubalanci ma’aikatar jin kai da ta bayyana sunayen mutanen da ake zargin mawakin ya hada baki da su.
Idan dai ba a manta ba a ranar Laraba ne hukumar ICPC ta fitar da sanarwa inda ta ce an tsare mawakin ne bisa zargin karkatar da kudaden N-Power.
Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa: “Mu, a daya bangaren, muna sake jaddada cewa D’banj ba shi da irin wannan damar ko kuma ya hada baki da wani jami’in gwamnati kan duk wata kullalliya mai cike da shakku. Zargin wani mummunan mafarki ne wanda dole ne a warware shi ta hanyar tabbatar da gaskiyar rashin laifin D’banj da ba a iya hukunta shi ba.”