Hukumar da ke yaki da almundahana da sauran lafukan da suka shafi cin hanci ta ICPC, ta ce, ta fara sabon bincike kan yadda aka aiwatar da ayyukan mazabu 712 a fadin johohin kasar 20.
Mai magana da yawun hukumar, Azuka Ogugua, ta ce, jihohin da za a gudanar da binciken ayyukan mazabun sun hadar da Kaduna da Jigawa da Sokoto da Katsina da Kwara da Niger da Kogi da wasu jihohin.
Ta kara da cewa ”a yayin da hukumar ta fara binciken tun shekarar 2019, manufar wannan sabon binciken shi ne bibiya game da hanyoyin da aka bi wajen bayar da kwagilar wasu zababbaun ayyukan mazabu a fadin kasar”.
“Manufar binciken shi ne tabbatar da cewa duka ayyukan da gwamnati ta fitar da kudi a kansu, an aiwatar da su a wuraren da aka tsara gudanar da su”, in ji Azuka