fidelitybank

ICPC ta fara bincike a kan jami’o’in Cotonoun da Benin

Date:

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC, a Najeriya ta ce ta fara bincike kan zargin samun shaidar karatun digiri ba bisa ka’ida ba a jami’ar Cotonou da ke jamhuriyar Benin.

ICPC ta bayyana hakan ne a shafinta na intanet, inda ta ce shugaban hukumar Dr. Musa Adamu Aliyu, SAN, ya kira wani taro a kan batun, a ranar Talata.

Binciken zai shafi jami’ar Ecole Superieure de Gestion et de Technologies (ESGT) ta Cotonou wadda ake zargin tana bayar da shaidar digiri a kasa da mako shida.

Hukumar ta ce za ta yi binciken don gano hanyoyin da ake bi domin yin badakalar da zummar kawo gyara a tsarin karatun.

Sannan za ta yi hadin guiwa da hukumomi na cikin gida da na waje domin tabbatar da ingancin shaidar karatun tare da zakulo wadanda ke da hannu a al’amarin.

Rahotan da ya bankado hakan ya yi zargin cewa ana samun kwalin karatun ba tare da bin hanyoyin da suka dace ba, kamar rashin gabatar da takardar bukatar yin karatu da rijista da karatun da kuma rashin rubuta jarrabawa.

Hakan na zuwa ne bayan gwamnatin Najeriyar ta sanar da dakatar da karbar shaidar digiri daga Cotonou da kuma Togo sakamakon badakalar.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp