Shugaban kungiyar Dillan Manfetur ta kasa masu zaman kansu, Alhaji Bashir Dan Malam ya tabbatar da cewa hutun da a ka shiga ne shi ne ya sanya a ke karancin man fetur a jihar Kano.
Bashir Dan Malam ya bayyana hakan ne a ganawarsa da manema labarai, cewa komai zai daidai ta dazarar an dawo daga hutu.
Ya kuma ce, halin da a ka tsinci kai na karancin rashin man fetur a Kano, ya na da nasaba ne da hutun da a ka shiga, amma kuma komai zai wuce.
Batun janye tallafin man fetur kuwa da gwamnatin tarayya ta yi, ya ce ba zai tofa albarkacin bakin sa ba, dangane da batun.