fidelitybank

Hungary ta tura sojoji don yakar ‘yan ta’addan Chadi

Date:

Majalisar dokokin Hungary ta amince da tura sojoji 200 zuwa ƙasar Chadi, domin inganta zaman lafiya da tsaro, da kuma yaƙi da ta’addanci.

Chadi, ƙasar da ke tsakiyar Afrika na fuskantar barazanar tsaro daga ƙungiyoyin masu aikata laifi.

A cewar ma’aikatar tsaron kasar, tura dakaru daga farkon 2024 zuwa Disamban 2025, zai kuma rage matsin lamba na kwararar bakin haure zuwa Turai.

A halin da ake ciki, majalisar ministocin kasar Chadi ranar Laraba, ta amince da wata doka da za ta yi afuwa ga mutanen da ke da hannu a zanga-zangar adawa da gwamnati ranar 20 ga Oktoban 2022.

Mutane akalla 50 ne suka mutu lokacin da ɗaruruwan masu zanga-zangar nuna adawa da gwamnatin Chadi suka yi arangama da jami’an tsaro.

Masu zanga-zangar dai na adawa ne da tsawaita wa’adin gwamnatin riƙon kwarya da shekaru biyu, inda suka zargi shugaban rikon kwaryar Janar Mahamat Idris Deby da neman ci gaba da zaman dafa’an a kan karagar mulki.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp