Majalisar dokokin Hungary ta amince da tura sojoji 200 zuwa ƙasar Chadi, domin inganta zaman lafiya da tsaro, da kuma yaƙi da ta’addanci.
Chadi, ƙasar da ke tsakiyar Afrika na fuskantar barazanar tsaro daga ƙungiyoyin masu aikata laifi.
A cewar ma’aikatar tsaron kasar, tura dakaru daga farkon 2024 zuwa Disamban 2025, zai kuma rage matsin lamba na kwararar bakin haure zuwa Turai.
A halin da ake ciki, majalisar ministocin kasar Chadi ranar Laraba, ta amince da wata doka da za ta yi afuwa ga mutanen da ke da hannu a zanga-zangar adawa da gwamnati ranar 20 ga Oktoban 2022.
Mutane akalla 50 ne suka mutu lokacin da ɗaruruwan masu zanga-zangar nuna adawa da gwamnatin Chadi suka yi arangama da jami’an tsaro.
Masu zanga-zangar dai na adawa ne da tsawaita wa’adin gwamnatin riƙon kwarya da shekaru biyu, inda suka zargi shugaban rikon kwaryar Janar Mahamat Idris Deby da neman ci gaba da zaman dafa’an a kan karagar mulki.