fidelitybank

Hungary ta ce ba za ta taimakawa Ukraine ba a fadan Rasha

Date:

Firaministan Hungary Viktor Orban, ya yi watsi da buƙatar Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky na neman ƙasar ta ba su makamai da kuma saka wa Rasha tsauraran takunkumai, yana mai cewa “hakan ya saɓa wa muradun Hungary”.

Orban ya ƙi amincewa da buƙatar ta Zelensky a wurin taron Majalisar Turai “saboda sun saɓa wa muradun Hungary”, a cewar wani magana da yawun gwamnatin Hungary cikin wata sanarwa.

“Hungary ba ta son ta goyi bayan wani ɓangare a yaƙin nan, saboda haka ba za ta bari a kai makamai Ukraine ba,” in ji Kovacs.

Orban ya ce ‘yan asalin Hungary da ke zaune a yammacin Ukraine za su shiga cikin zullumi idan ƙasarsu ta kai wa Ukraine ɗin makamai.

Hungary wadda mamba ce a ƙawancen tsaro na Nato, ta ƙi aika wa Ukraine makamai da kuma ƙyale ta ta bi sararin samaniyarta. Sai dai ta bar rabin miliyan na ‘yan Ukraine sun shiga ƙasarta.

Orban ɗan jam’iyyar kishin ƙasa, ya ƙulla ƙawance da Shugaban Rasha Vladimir Putin a ‘yan shekarun nan.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp