Firaministan Hungary Viktor Orban, ya yi watsi da buƙatar Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky na neman ƙasar ta ba su makamai da kuma saka wa Rasha tsauraran takunkumai, yana mai cewa “hakan ya saɓa wa muradun Hungary”.
Orban ya ƙi amincewa da buƙatar ta Zelensky a wurin taron Majalisar Turai “saboda sun saɓa wa muradun Hungary”, a cewar wani magana da yawun gwamnatin Hungary cikin wata sanarwa.
“Hungary ba ta son ta goyi bayan wani ɓangare a yaƙin nan, saboda haka ba za ta bari a kai makamai Ukraine ba,” in ji Kovacs.
Orban ya ce ‘yan asalin Hungary da ke zaune a yammacin Ukraine za su shiga cikin zullumi idan ƙasarsu ta kai wa Ukraine ɗin makamai.
Hungary wadda mamba ce a ƙawancen tsaro na Nato, ta ƙi aika wa Ukraine makamai da kuma ƙyale ta ta bi sararin samaniyarta. Sai dai ta bar rabin miliyan na ‘yan Ukraine sun shiga ƙasarta.
Orban ɗan jam’iyyar kishin ƙasa, ya ƙulla ƙawance da Shugaban Rasha Vladimir Putin a ‘yan shekarun nan.