fidelitybank

Hukuncin Kotu: Magoya baya ku kwantar da hankalin ku mu na nazari a kai

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya yi kira ga magoya bayansa a jam’iyyar APC mai mulki a jihar da su kwantar da hankalinsu, su kuma bi hanyar zaman lafiya da bin doka da oda.

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a matsayin martani ga hukuncin da wata babbar kotun Abuja ta yanke ranar Juma’a, wanda ya nuna goyon bayan wani bangare na jam’iyyar a jihar.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Muhammad Garba ya fitar, wadda PlatinumPost ta samu a ranar Juma’a, gwamnan ya ce” Tunda lamarin na cikin jam’iyya ne, gwamnati da jam’iyyar APC a halin yanzu muna nazari kan lamarin, domin samun mafita”.

Gwamna Ganduje ya kuma umurci jami’an tsaro da kada su lamunci rashin bin doka da oda, domin gwamnati ba za ta amince da duk wani aika-aika da ta’addanci ko tashin hankali a wani yanki na jihar ba, da sunan siyasa ko wani fage.

Sanarwar ta kuma nuna godiya ga ‘yan jam’iyyar a dukkan matakai da sauran masu ruwa da tsaki bisa jajircewar da su ka nuna wajen marawa jam’iyyar baya.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp