fidelitybank

Hukuncin kotu a kan CBN nasara ce ga ‘yan Najeriya – Gwamnan Zamfara

Date:

Gwamna Bello Mohammed na jihar Zamfara ya ce, hukuncin da Kotun Koli ta yi kan karɓar tsofaffin kuɗin naira da kuma bin hukuncin da Babban Bankin ƙasa CBN, ya yi nasara ce ga dukkanin ƴan Najeryia.

Gwamnan wanda shi da takwarorinsa na jihar Kaduna da Kogi suka fara shigar da ƙara kan wa’adin da Babban bankin ya sa na daina amfani da tsofaffin takardun kudin naira 200 da 500 da kuma 1,000 kafin wasu gwamnonin su mara musu baya a shari’ar,

ya ce a yanzu gaskiya ta yi halinta, duk da cewa a da ana zarginsu da cewa sun ɗauki matakin ne saboda zaɓen shugaban ƙasa, duk kuwa da cewa a zahiri take ƴan ƙasar na shan wuya saboda canjin.

Karanta Wannan: Sojoji da ‘Yan Banga sun dakile harin ‘yan bindiga a Zamfara

Ya kara da cewa a yanzu ƴan Najeriya za su samu sa’ida a kan wannan lamari, yana mai cewa suna fatan ganin an samar da ƙarin takardun kuɗi a tsakanin jama’a domin sauƙaƙa wahalar da ake ciki, yayin su kuma waɗanda suke da tsofaffin takardun ba za su yi asara ba.

Matawalle ya kuma yaba wa Shugaba Muhammadu Buhari a kan yadda ya nesanta gwamnatinsa daga matakin Babban bankin na ƙin mutunta hukuncin Kotun Ƙoli na matsar da wa’adin daina amfani da tsofaffin takardun kuɗin na naira har zuwa ranar 31 ga watan Disamba na wannan shekara.

Tun a ranar 3 ga watan nan na Maris Kotun Ƙolin Najeriya ta yanke hukuncin ɗaga wa’adin daina amfani da tsofaffin takardun kuɗin amma Babban Bankin ya yi shiru kan ambata cewa ya amince da hukuncin, wanda hakan ya sa jama’a suka shiga tsaka-mai-wuya, kan amfani da tsofaffin kuɗin.

Halin da jama’a suka shiga na ƙunci da sukar gwamnati da ake yi na ƙin magana kan lamarin wasu ke ganin ya tilasta wa fadar shugaban ƙasar a jiya Litinin ta fito ta nesanta kanta ga ƙin bin umarnin, abin da ya sa a yanzu Bankin ya fito ya bayar da kai.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp