Shekara ɗaya bayan wani mummunan harin da jirgin saman sojin Najeriya ya kai a garin Rukubi na jihar Nasarawa da ya yi sanadin mutuwar mutane 40, waɗanda abin ya shafa da iyalansu har yanzu na jiran a yi musu adalci.
Shugaban ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce hukumomin ƙasar sun gaza wajen tabbatar da adalci da kuma bin diddigin harin da aka kai.
Sanusi ya soki yadda ake amfani da hare-hare ta sama wajen tabbatar da doka da oda, yana mai cewa hakan ya saɓa wa doka, haramun ne da kuma yin amfani da karfi ne fiye da kima, yana mai jaddada cewa tamkar tsawaita rashin adalci ne ga iyalan waɗanda abin ya shafa.
“Rashin hukunta sojojin da ke da alhakin kai irin wannan harin kan fararen hula na nuna rashin mutunta rayuwar ɗan’adam da kuma ƙara ƙarfafa gwiwar kai irin wannan harin nan gaba tare da kuma ƙara jefa mutanen da ke zaune a yankunan karkara, waɗanda ke fama da tashe-tashen hakula cikin hatsari mai girma.” in ji shi.
“Hare-haren jiragen sama tare da yawaitar kashe-kashen mutane ba bisa ƙa’ida ba sun zama daya daga cikin jerin manyan laifukan take haƙƙin bil’adama na baya-baya nan da sojojin Najeriya ke yi.”
“Dole ne mahukuntan Najeriya su bai wa sojoji umarni da su rika bai wa rayuwar fararen hula fifiko da muhimanci da kuma mutunta hakkin dan’adam a koda yaushe yayin gudanar da dukkan ayyukan tsaro. Dole ne gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta gudanar da bincike mai zaman kansa, ba tare da nuna son kai ba, kuma mai inganci, kan harin da aka kai wa Rukubi ta sama, da ma wasu da dama da suka haddasa kashe-kashe ba bisa ka’ida ba.
“Ya kamata a gurfanar da wadanda ake zargi da hannu a gaban shari’a ta hanyar shari’a ta gaskiya, ciki har da wadanda ke da alhakin daidaikun mutane da na sojoji da manyan kwamandojin sojoji.”