Hukumar Zakka da Hubsi ta jihar Kano ta rabawa mabukata 100 zakkar kudi Naira 10,000 kowannan su, domin kyautata rayuwarsu tare da rage musu radadin matsin rayuwa da a ke fuskanta a wannan lokaci.
Da ya ke zantawa da manema labarai shugaban hukumar, Sheikh Yusuf Usman Makwarari, ya ce wani bawan Allah mai suna, Alhaji Umar Abba Muhd ne ya kaiwa hukumar zakkarsa ta wannan shekarar.
Ya kuma ce, “Mutumin ya kawo Zakka a dai-dai lokacin da al’umma su ke cikin tsananin bukata, saboda matsin rayuwa da a ke fama da shi. Wannan bawan Allah da ya kawo wannan kudin har Naira Miliya daya, domin rabawa mabukata, saboda haka muna kira ga mawadatan da ke jihar Kano da su rinka kawowa hukumar Zakka zakkarsu, domin da hakan sai kaga Allah ya yi mana maganin matsalolin da a ke ciki”. In ji Sheikh Makwarari.
A jawabinsa darakta Janar na hukumar Zakka ta jihar Kano, Alhaji Safyan Ibrahim Gwagwarwa, ya ce, hukumar ta yi tsari na musamman wajen zabo wadanda su ka amfana da Zakkar