fidelitybank

Hukumar zaɓe ta fitar da sunayen ƴan takarar gwamna a Osun

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), a ranar Talata ta fitar da bayanan sunayen ‘yan takara a zaben gwamnan jihar Osun.

Hukumar a cikin wata sanarwa da kwamishinan kasa kuma shugaban kwamitin wayar da kan jama’a da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye, ya fitar a Abuja, ya ce, an buga jerin sunayen ne a ofisoshin INEC na jihar da na kananan hukumomin jihar Osun kamar yadda doka ta tanada.

Okoye ya ce, an buga jerin sunayen ne bisa bin dokar zabe ta 2022, bayan da jam’iyyun siyasa suka miƙa sunayen ‘yan takara.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa, ‘yan takara 15 da aka buga, yayin da babu daya daga cikin ‘yan takarar gwamnan da bai amince ba, shida daga cikin mataimakan gwamna mata ne.
‘Yan takarar da aka buga sun hada da Adegboyega Oyetola na jam’iyyar APC , Adeleke Nurudeen na jam’iyyar PDP da Omigbodun Akinrinola na SDP.

Ya tunatar da jam’iyyun siyasa cewa, a karkashin sashe na 32(2) na dokar zabe ta 2022, duk jam’iyyar da ta lura cewa, sunan dan takararta ya bata a cikin jerin sunayen za ta sanar da Hukumar a rubuce.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp