Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Kano ta kama manajojin gidajen man fetur hudu, bisa zargin sayar da mai fiye da farashin da aka kayyade na Naira 165 kan kowace lita.
Hukumar ta kama ma’aikatan gidajen mai biyu kan lamarin, wanda a ka kama su ne bayan samun korafe-korafe daga jama’a cewa, duk da karancin man da ake fama da shi wasu gidajen mai na sayarwa kan Naira 200 zuwa Naira 208 a jihar Kano.
Hukumar da ke karbar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano (PCACC), da shugaban ta Mahmoud Balarabe ke jawabi a wani taron manema labarai da ya gudana a ofishinsa a ranar Talata, 15 ga watan Fabrairu. Mukaddashin shugaban hukumar, Mahmoud Balarabe, ya ce, an kama mutanen ne a gidajen mai mabanbanta da ke cikin garin Kano.
Ya ce, “Daya mutumin kuma ma’aikacin mai ne, kuma mun kama shi ne bayan manajan na sa ya haura katanga ya gudu. Akwai gidan mai da muka gano cewa, sun riga sun siyar da lita 18,000 kan Naira 200, inda muka samu Naira 630,000 a kan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba. An gano dayan gidan mai ya boye sama da lita 4,000. Mun tursasa su ci gaba da sayar wa mutane lita 4,000 da su ka boye.” A cewar Mahmoud in ji BBC.