fidelitybank

Hukumar NEMA ta fara kai agaji Borno

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), ta ce ta fara kai agaji domin kwashe mutanen da ambaliyar ruwa ta ɗaiɗaita a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Ambaliyar ta biyo bayan fashwar madatsar ruwa.

Wata sanawar da babbar darektar hukumar Zubaida Umar ta fitar a shafinta na X, ta ce sun kuma fara shirye-shiryen tallafa wa mutanen da lamarin ya shafa da abinci, matsuguni da kuma magaunguna.

Yankunan da ambaliyar ta shafa sun haɗa da Shehuri, rukunin gidaje da ke G.R.A, Gambomi, Budum, Bulabulin, Adamkolo, Millionaires Quarters, kasuwar Monday Market da kuma Gwange.

NEMA ta ce gwamnatin jihar Borno ta buɗe sansanin Bakassi domin tsugunar da mutanen da ambaliyar ta shafa.

Ta ce suna aiki da hukumar ba da agaji reshen jihar ta Borno domin tallafa wa mutanen da ke cikin sansanin.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp