Hukumar leken asiri ta Amurka, CIA, ta tura wasu jami’anta guda biyar hutun dole sakamakon binciken da ake yi kan yunkurin da aka yi na halaka tsohon shugaban kasar kuma ɗan takarar shugabancin ƙasar na jam’iyyar Republican, Donald Trump a watan jiya.
Majiyoyi sun ce ɗaya daga cikinsu shi ne shugaban wani reshen hukumar .
Hukumar leken asirin na fuskantar bincike kan gazawarta wajen hana maharin samun isa wurin da Trump yake gangamin yakin neman zabe.
Harbin dai ya samu tsohon shugaban a kunne sannan mutum ɗaya ya mutu, biyu kuma sun jikkata, a harin.
Jami’an tsaro sun kashe maharin a lokacin.