fidelitybank

Hukumar Kwastam ta dakatar da aikin sintiri na hadin gwiwa

Date:

Hukumar Kwastam ta sanar da dakatar da aikin sintirin haɗin gwiwar jami’an tsaro na bakin iyakokin ƙasar, wato Joint Border Patrol Team (JBPT).

Kakakin hukumar, Abdullahi Maiwada ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, inda ya ce an ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

A ranar 11 ga Disamba ne majalisar wakilai ta ba kwamitinta na kwastam umarnin gudanar da bincike kan ayyukan jami’an kwastam a bakin iyakokin ƙasar bayan zarge-zargen almundahana da cin zarafin ƴanƙasar, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Amma kakakin rundunar ya ce hukumar ta ɗauki wannan matakin ne a yunƙurinta na inganta tsaron bakin iyakokin domin fuskantar 2025.

Maiwada ya ƙara da cewa dakatar da jami’an ba zai zama barazana ga tsaron bakin iyakokin ƙasar ba, inda ya ƙara da cewa za su ɗauki matakin zamanantar da ayyukan hukumar domin tabbatar da tsaron ƙasar.

Asali an kafa dakarun haɗin gwiwar ne a ƙarƙashin kulawar ofishin NSA domin yaƙi da fasaƙauri da kwarorowar baƙin haure da wasu manyan laifuka.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp