fidelitybank

Hukumar kwallon kafa ta Afrika CAF ta baiwa Najeriya maki uku a kan Libiya da cin tarar ta

Date:

Hukumar kula da ƙwallon ƙafa ta Afrika CAF ta bai wa Najeriya maki uku da ƙwallo uku kan Libya, a wasan da ƙasashen biyu ba su buga ba, bayan da aka zargi jami’an Libya da karkatar da jirgin ‘yan wasan Najeriya zuwa wani filin jirgi a ƙasar.

Tun da farko an tsara karawa tsakanin ƙasashen biyu domin neman gurbin shigar gasar Afirka ta 2025.

A hukuncin da ta sanar a shafinta na Intanet, CAF ta bayyana cewa an sami hukumar ƙwallon ƙafa ta Libya da laifin karya sashe na 31 na dokokin gasar cin kofin nahiyar Afrika da kuma sashe na 82 da 151 na dokokin CAF.

Haka kuma hukumar ta CAF ta ci tarar hukumar ƙwallon ƙafar Libya dala 50,000.

Hukuncin na CAF na zuwa ne kwanaki kaɗan, bayan shugaban hukumar Patrice Motsepe, ya ce hukumar ta himmatu wajen ganin tabbatar da daidaito a harkar ƙwallon ƙafa a nahiyar.

Matakin ya kawo ƙarshen yunƙurin neman gurbin shiga gasar da Libya ke yi, inda ta ƙare da maki ɗaya kacal a wasanni huɗu, yayin da Najeriya wanda ta zo ta biyu a gasar da ta gabata, ke da maki 10, kuma ta kusa tabbatar da gurbinta a gasar da ake gudanarwa bayan shekara biyu-biyu.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp