fidelitybank

Hukumar kwallon kafa ta Afrika CAF ta baiwa Najeriya maki uku a kan Libiya da cin tarar ta

Date:

Hukumar kula da ƙwallon ƙafa ta Afrika CAF ta bai wa Najeriya maki uku da ƙwallo uku kan Libya, a wasan da ƙasashen biyu ba su buga ba, bayan da aka zargi jami’an Libya da karkatar da jirgin ‘yan wasan Najeriya zuwa wani filin jirgi a ƙasar.

Tun da farko an tsara karawa tsakanin ƙasashen biyu domin neman gurbin shigar gasar Afirka ta 2025.

A hukuncin da ta sanar a shafinta na Intanet, CAF ta bayyana cewa an sami hukumar ƙwallon ƙafa ta Libya da laifin karya sashe na 31 na dokokin gasar cin kofin nahiyar Afrika da kuma sashe na 82 da 151 na dokokin CAF.

Haka kuma hukumar ta CAF ta ci tarar hukumar ƙwallon ƙafar Libya dala 50,000.

Hukuncin na CAF na zuwa ne kwanaki kaɗan, bayan shugaban hukumar Patrice Motsepe, ya ce hukumar ta himmatu wajen ganin tabbatar da daidaito a harkar ƙwallon ƙafa a nahiyar.

Matakin ya kawo ƙarshen yunƙurin neman gurbin shiga gasar da Libya ke yi, inda ta ƙare da maki ɗaya kacal a wasanni huɗu, yayin da Najeriya wanda ta zo ta biyu a gasar da ta gabata, ke da maki 10, kuma ta kusa tabbatar da gurbinta a gasar da ake gudanarwa bayan shekara biyu-biyu.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp