Hukumar kula da ƙwallon ƙafa ta Afrika CAF ta bai wa Najeriya maki uku da ƙwallo uku kan Libya, a wasan da ƙasashen biyu ba su buga ba, bayan da aka zargi jami’an Libya da karkatar da jirgin ‘yan wasan Najeriya zuwa wani filin jirgi a ƙasar.
Tun da farko an tsara karawa tsakanin ƙasashen biyu domin neman gurbin shigar gasar Afirka ta 2025.
A hukuncin da ta sanar a shafinta na Intanet, CAF ta bayyana cewa an sami hukumar ƙwallon ƙafa ta Libya da laifin karya sashe na 31 na dokokin gasar cin kofin nahiyar Afrika da kuma sashe na 82 da 151 na dokokin CAF.
Haka kuma hukumar ta CAF ta ci tarar hukumar ƙwallon ƙafar Libya dala 50,000.
Hukuncin na CAF na zuwa ne kwanaki kaɗan, bayan shugaban hukumar Patrice Motsepe, ya ce hukumar ta himmatu wajen ganin tabbatar da daidaito a harkar ƙwallon ƙafa a nahiyar.
Matakin ya kawo ƙarshen yunƙurin neman gurbin shiga gasar da Libya ke yi, inda ta ƙare da maki ɗaya kacal a wasanni huɗu, yayin da Najeriya wanda ta zo ta biyu a gasar da ta gabata, ke da maki 10, kuma ta kusa tabbatar da gurbinta a gasar da ake gudanarwa bayan shekara biyu-biyu.