fidelitybank

Hukumar kula da jiragen ƙasa ta dakatar jigila daga Abuja zuwa Legas

Date:

Hukumar Kula da Jiragen Kasa ta Najeriya ta dakatar da jigila tsakanin Abuja zuwa Kaduna, bayan da wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan wani jirgin kasa da ke kan hanyarsa ta zuwa Kaduna ranar Litinin da daddare.

A wani sako da hukumar ta wallafa a shafinta na twitter da safiyar nan, ta ce, “saboda wasu dalilai da ba mu shirya musu ba, mun dakatar da jigilar jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna. Nan gaba za mu yi muku karin bayani idan akwai”.

Rahotanni daga Najeriya na cewa an sace wasu fasinjoji da ba a bayyana adadinsu ba daga wani jirgin kasa da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna a yammacin ranar Litinin.

Shaidu sun ce, jirgin ya kauce daga kan hanyarsa bayan fashewar wani abu a kan hanyarsa.

Rahotanin sun ce an samu asarar rayuka yayin da wasu da dama suka jikkata.

An kai wa jirgin kasan mai dauke da fasinjoji kusan 1,000, harin ne da misalin karfe 8 na dare.

Fasinjoji da kuma ‘yan uwan wasu fasinjojin sun shaida wa BBC cewa, lamarin ya yi matukar muni kuma har yazu ba a san takamaiman mutanen da lamarin ya shafa ba.

Wani fasinja ya shaida mana cewa bayan jirgin ya tsaya, ‘yan bindiga sun kewaye shi tare da bude wuta.

Mutane sun sunkuya kasa domin samun mafaka kuma daga nan ne maharan suka nufi hanyar jirgin, inda suka harbe fasinja daya a kusa da inda suka yi awon gaba da mutanen da ba a san adadinsu ba, in ji shi.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp