Gwamnatin jihar Kano ta kama mabarata sama da 300 maza da mata yara da manya a titunan birnin Kano.
Shugaban hukumar hana barace-barace a jihar Kano, Malam Albakari Mika’il ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai.
Ya ce“Mafi yawan wadanda mu ka kama ba Almajirai ba ne da ke zuwa makaranta ba. Mutane ne masu yin bara a tituna, kuma gwamnati ba za ta saurarawa duk wanda ta kama sau biyu ba, za mu mika su ga kotu, domin ta yanke musu hukunci kamar yadda ya dake. Su kuma yaran za mu mayar da wasu gaban iyayensu wasu kuma musamman wadanda aka same su na shaye-shaye za a mika su ga hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi da kuma mika wasunsu ga rundunar Æ´an Sanda”. In ji Albakari.
Malam Albakari ya kuma tabbatar da cewa, hukumar za ta cigaba da kama masu bara a kwaryar birnin Kano da kewaye domin tsaftace Kano.