Hukumar alhazai ta kasa, ta mayar da hukumomin alhazai na jihohin da ba su samu cikakkiyar kulawar hukumar ba lokacin aikin hajjin da ya gabata na 2023.
Cikin wani saƙo da Nahcon ɗin ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce kuɗin wanda ya kai naira biliyan 5.3, ya shafi kamfanonin shirya tafiye-tafiyen da hukuomin alhazan jihohin da ba su kulawar da ta dace ba a lokacin aikin hajjin da ya gabata.
Wasu jihohin ƙasar da ma kamfanonin shirya tafiye-tafiye sun bayyana ƙorafe-ƙorafensu bayan kammala aikin hajin kan abin da suka kira rashin ingancin aiki da rashin kulawa daga hukumar alhazai ta ƙasar.
Inda wasu da dama suka zargi hukumar alhazan ƙasar da karkatar da wani ɓangare na kuɗaɗen tallafin aikin hajji da gwamnatin tarayya ta bayar, wani abu da wasu ke alaƙanta wa da korar tsohon shugaban hukumar alhazan ƙasar, Malam Jalal Ahmad Arabi.