Hukumar alhazan Najeriya, NAHCON, ta ce ta kammala jigilar maniyyatan jihohin ƙasar biyar a jigilar maniyytan ƙasar da take yi zuwa ƙasa mai tsarki.
Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ya nuna ce kawo yanzu hukumar ta kammala kwashe maniyyan jihohin Kogi da Nasarawa da Edo da Oyo da kuma jihar Ogun.
Haka kuma hukumar ta ce ta kammala kwashe maniyyatan da suka biya ta hukumar rundunar sojin ƙasar.
Hukumar ta kuma ce kawo yanzu ta yi jigilar maniyyatan ƙasar fiye da 19,700.
Nahcon ɗin ta kuma ce tana dab da kammala kwashe maniyytan jihohin Yobe da Banchi da Osun da Legas da Kebbi da Abuja.